1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Burkina Faso ta rufe shafin DW kan kwarmata kisan kiyashi

April 29, 2024

A daidai lokacin da Burkina Faso ke yinkurin hana ayyukan kafafen yada labaran ketare a kasar, kasashen Amurka da Burtaniya sun bukaci gwamnatin sojin kasar da su gudanar da bincike kan kashe fararen hula kimanin 223.

https://p.dw.com/p/4fKEG
Tambarin Deutsche Welle
Tambarin Deutsche WelleHoto: Marc John/imago images

Dama kungiyar Human Rights Watch ta yi zargin sojoji da halaka mutane sakamakon  taimaka wa masu ikrarin jihadi da ke dauke da makamai.

Karin bayani: Burkina Faso ta yi fatali da zarge-zargen Human Rights Watch 

Sai dai hukumomin kasashen Amurka da Burtaniya sun nuna damuwa dangane da kisan na fararen hula da ake zargin sojojin kasar da aikatawa, a wata sanarwar hadin gwiwa da gwamnatocin kasashen biyu suka fitar.

Karin bayani: Ana zargin sojojin Burkina Faso da kashe fararen hula 223 

Hukumomin Burkina Faso sun dakatar da ayyukan kafafen yada labaran kasashen ketare a kasar ciki har da shafin Internet na Deutsche Welle na kasar Jamus da jaridun Faransa da suka hadar da  Le Monde da Ouest-France,  har ma da jaridar The Guardian ta kasar Burtaniya da kuma wasu kamfanin dillancin labarai na Afirka.