1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Finidi ya zama sabon kocin kungiyar kwallon kafa ta Najeriya

April 29, 2024

Hukumar kwallon kafa ta Najeriya ta nada tsohon 'dan wasan Ajax Amsterdam Finidi George a matsayin sabon mai horas da babbar kungiyar Super Eagles, wanda hakan ya kawo karshen cece-kuce game da maye gurbin Jose Peseiro.

https://p.dw.com/p/4fKJ8
Shugaban Najeriya Bola Tinubu da tawagar Super Eagles karkashin jagorancin tsohon mai horas da kungiyar Jose Peseiro.
Shugaban Najeriya Bola Tinubu da tawagar Super Eagles karkashin jagorancin tsohon mai horas da kungiyar Jose Peseiro.Hoto: Ubale Musa/DW

A cikin wata sanarwa da hukumar gudanarwar ta NFF ta fitar a Abuja, ta ce dukkan mambobin kwamitin sun amince da nadin Finidi George 'dan shekara 52 da zai jagoranci kungiyar ta Super Eagles.

Karin bayani: Najeriya ta sanar da makomar kocin Super Eagles 

Da farko hukumar kwallon kafar Najeriya ta so ta nada mai horaswa daga kasashen ketare, amma ma'aikatar da ke kula da wasanni ta Najeriya ta nuna rashin amincewa sakamakon karancin kudi biyan Koci tare da neman a nada mai horaswa daga Najeriya. An fara ambato sunan Daniel Amokachi kafin a samu daidaito a kan Finidi George.

Karin bayani: Najeriya: Kalubalen da ke a gaban Super Eagles 

Babban kalubalen da ke gaban sabon mai horas da kungiyar ta Super Eagles shi ne tabbatar da cewa Najeriya ta cancanci kai wa gasar cin kofin duniya FIFA 2026, musamman a wasannin share fagen shiga, inda Super Eagles za ta kalubalanci kasashen Arika ta Kudu da Jamhuriyar Benin a watan Yunin 2024.